DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sudan ta kudu ta soki Amurka kan hana ‘yan kasarta Biza

-

Google search engine

Sudan ta Kudu ta bayyana rashin jin daɗinta kan matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na janye biza ga dukkan ’yan ƙasar, tana mai cewa hakan ba gaskiya ba ne kuma ya samo asali ne daga kuskuren tantance ɗan wata ƙasa.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya sanar da wannan mataki bisa zargin cewa Sudan ta Kudu ta ki karɓar ’yan ƙasarta da aka kora daga Amurka.

Sai dai Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan ta Kudu ta ce batun ya danganci wani ɗan ƙasar Kongo da aka dauka a matsayin ɗan Sudan ta Kudu, wanda yanzu haka aka mayar da shi Amurka don sake duba lamarin.

Wannan shi ne karon farko tun dawowar Shugaba Donald Trump kan mulki da Amurka ke kakabawa wata ƙasa takunkumin hana biza ga duk masu fasfo dinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Trump ya shigar da kara kan BBC, yana neman diyyar dala bilyan 5

Shugaban Amurka Donald Trump ya shigar da kara a kotu yana neman diyya ta dala bilyan 5 (kimanin fam biliyan 3.7) kan BBC, bisa zargin...

Marigayi Buhari ya nuna cewa mulki amana ce, ba hanyar tara dukiya ba – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana marigayi Shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin jagora mai karfin hali cikin natsuwa da kan ladabi, kuma mai...

Mafi Shahara