DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku karbo Nijeriya daga hannun dattijan da ke shugabancin kasar – Femi Falana ya shawarci matasa

-

Fitaccen lauya mai rajin kare hakkin dan’adam, Femi Falana, SAN, ya shawarci matasan Nijeriya da su karbo kasar daga hannun dattijai ta dawo hannunsu.
Dan gwagwarmaya Falana ya bayar da wannan shawara ne a birnin Legas, yayin taron shekara-shekara karo na shida na jagorancin matasa, wanda aka lakaba wa suna ‘Resilience, Innovation, Social Responsibility and Entrepreneurship (RISE 2025).
Falana ya ce abubuwa ba su kasance kamar yadda suke a da ba, saboda haka ya zama wajibi matasa su kwato kasarsu kuma su sake fasalta ta yadda ya kamata.
Ya kara da cewa matasa suna shan wahala sakamakon halin da kasar ta shiga, saboda haka akwai bukatar matasa su tashi tsaye don zage damtse su yi abin da ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara