DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Zamfara ta biya kamfanin KEDCO bashin kudin lantarki Naira bilyan daya

-

Gwamnatin jihar Zamfara ta biya bashin Naira biliyan 1 da kamfanin rarraba wutar lantarki na Kaduna,KEDCO ke bi.

Gwamnatin ta kuma kara wa’adin sabuwar hukumar samar da wutar lantarki ta jihar Zamfara, ZEA, da inganta samar da wutar lantarki ga al’ummomin da ke jihar.

Google search engine

Babban sakataren hukumar ZEA, Muzammil Idris ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN a Gusau, ranar Alhamis.

Idris ya ce gwamnatin Dauda Lawal ta kubutar da jihar daga basussukan da ke zama cikas ga ci gaban da ake sa ran za a samu na ayyukan gwamnati domin ci gaban tattalin arzikin jihar.

A cewarsa, tuni hukumar ta yi tsarin aiki na shekaru 10 da dabarun aiwatarwa domin samun samun sauki ga al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara