DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Zamfara ta biya kamfanin KEDCO bashin kudin lantarki Naira bilyan daya

-

Gwamnatin jihar Zamfara ta biya bashin Naira biliyan 1 da kamfanin rarraba wutar lantarki na Kaduna,KEDCO ke bi.

Gwamnatin ta kuma kara wa’adin sabuwar hukumar samar da wutar lantarki ta jihar Zamfara, ZEA, da inganta samar da wutar lantarki ga al’ummomin da ke jihar.

Google search engine

Babban sakataren hukumar ZEA, Muzammil Idris ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN a Gusau, ranar Alhamis.

Idris ya ce gwamnatin Dauda Lawal ta kubutar da jihar daga basussukan da ke zama cikas ga ci gaban da ake sa ran za a samu na ayyukan gwamnati domin ci gaban tattalin arzikin jihar.

A cewarsa, tuni hukumar ta yi tsarin aiki na shekaru 10 da dabarun aiwatarwa domin samun samun sauki ga al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara