DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NAHCON ta saka ranar da maniyyata aikin hajjin Nijeriya na 2025 za su fara tashi zuwa Saudiyya

-

Hukumar alhazai ta kasa NAHCON a cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yada labaran hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar, ta tunatar da shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi cewa hukumar na yin shiri na karshe kafin a fara jigilar mahajjata daga ranar ranar 22 ga watan Afrilu 2025.

Shugaban hukumar Farfesa Abdullah Saleh Usman wanda ya gana sakatarorin hukumomin, ya yi kira ga shugabannin da su ci gaba da wayar da kan alhazai wajen yin rigakafi tare da tabbatar da yin duk wasu abubuwa da ake bukata.

A yayin taron an bayyana cewa jirgin Air Peace zai dauki alhazai 5,128 daga jihohin Abia, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Ondo, Rivers, Taraba da Taraba.

Sai kuma kamfanin FlyNas an ware masa maniyyata 12,506 daga Abuja, Kebbi, Lagos, Ogun, Osun, Sokoto da Zamfara, yayin da kamfanin Max Air zai yi jigilar alhazai daga jihohin Bauchi, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kwara, Oyo da Plateau.

Kamfanin Umza kuwa zai yi jigilar maniyyata 10,163 daga jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Neja da Yobe.

Sanarwar ta ce kusan alhazai 43,000 ne za su sauka a kasa mai tsarki domin yin ibadar aikin hajjin shekarar 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara