DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wajibi a sauya yadda ake juya jam’iyyun siyasa a Nijeriya – Abbas Tajudden

-

Kakakin Majalisar Wakilai ta Tarayya, Hon. Tajudeen Abbas, ya bukaci a inganta tsarin jam’iyyu a Najeriya domin su daina zama tamkar kamfanonin kasuwanci da shugabanninsu ke amfani da su don ribar kansu.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN yace taron bitar wanda ya gudana a Abuja kan kudirin dokar gyaran jam’iyyu, Cibiyar bada taimakon Zabe ta Turai (ECES) ce ta shirya tare da hadin gwiwar YIAGA Africa da Cibiyar Kukah, Abbas – wanda Hon. Ishaya Lalu ya wakilta – ya ce dole ne a kara kaimi wajen sanya jam’iyyu su rika aiki da tsari da manufa.

Google search engine

Ya ce, duk da cewa Najeriya na bin tsarin mulkin shugabanci irin na Amurka, akwai tazara mai girman gaske wajen yadda ake rajista da kaka-gida da masu kudi kanyi wajen zuba jari a harkokin jam’iyyu.

Kakakin majalisar ya nuna damuwa da yadda yawancin jam’iyyun Najeriya ke fama da rashin tsari da akida, wanda hakan ke haddasa sauya sheka da karancin amincewar jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dokokin Bénin ta amince da kara wa’adin mulki zuwa shekaru 7

’Yan majalisar dokokin Benin sun amince da sabuwar dokar gyaran kundin tsarin mulki da ke tsawaita wa’adin mulkin shugaban ƙasar daga shekaru biyar zuwa bakwai. Gidan...

Na dauki matakin doka ne domin bin hakkina a PDP – Sule Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya ce ya kai kara kotu ne domin kare haƙƙinsa a jam’iyyar PDP, tare da jaddada cewa ba zai...

Mafi Shahara