DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

-

Wadanda abin ya shafa sun yi aiki ne a lokuta daban-daban tsakanin shekarar 2014 zuwa 2024 a lokacin mulkin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, amma ba su samu hakkokinsu ba tsawon lokaci.

A cewar mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Malam Ibrahim Adam, an tsara raba kudaden ne a matakai uku daga watan Afrilu zuwa Yuni 2025, inda ya ce matakin wani bangare ne na sake farfado da mutuncin wadanda suka taba hidimtawa al’umma a jihar.

Tsofaffin jami’an kananan hukumomi da abin ya shafa sun nuna godiya da jin daɗi game da wannan mataki, suna mai cewa hakan ya tabbatar da adalci da kishin jama’a daga bangaren gwamnatin Abba Kabir Yusuf.

Wannan mataki na daga cikin manufofin da gwamnatin ta Kano tace tana dauka gyaran kura-kuran da ta gada daga mulkin baya da kuma kafa sabuwar hanyar da ke cike da gaskiya, adalci da mutunta na kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara