DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

-

Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin jam’iyyar sun shirya wani muhimmin taro a ranar 11 ga watan Mayu, domin tunkarar kalubalen da ke barazana ga makomar jam’iyyar, musamman abun da ya shafi yawaitar sauya shekar da ke ci gaba da addabar jam’iyyar.

Wani amintaccen mamba daga cikin kwamitin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ne ya tabbatar wa jaridar PUNCH cewa shugabannin jam’iyyar da gwamnonin PDP za su gana a ranar 11 ga watan Mayu domin tattauna matsalolin da ke damun jam’iyyar.

Google search engine

Majiyar ta bayyana cewa taron zai fi mayar da hankali ne kan tsara dabarun dakile ci gaba da ficewar wasu jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar, da warware matsalar da ta shafi kujerar Sakataren Jam’iyyar na Kasa, da kuma wasu muhimman batutuwa da ke ci gaba da addabar jam’iyyar a fadin kasar.

Ana kallon wannan taro a matsayin wani mataki na sake farfado da jam’iyyar tare da dunkulewa domin tinkarar zaben 2027 da ke tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Mafi Shahara