DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilai ta gayyaci ministocin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki da gwamnan CBN kan kin biyan ‘yan kwangila tun Oktoban 2024

-

Majalisar Wakilai ta Tarayya a ranar Alhamis ta gayyaci Ministan Kudi kuma Ministan na tarayya, Wale Edun; ministan tsare-tsaren tattalin arziki da kasafin kudi, Sanata Atiku Bagudu; da kuma Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Olayemi Cardoso, domin bayyana dalilin kin biyan ’yan kwangilar da suka yi aiki da ma’aikatun gwamnati tun daga watan Oktoban shekarar 2024.

Hakazalika, Majalisar ta gayyaci Akanta-Janar na Tarayya da Audita-Janar domin su bayyana tare da sauran jami’an gwamnati a gaban Majalisar a ranar Talata, 13 ga watan Mayu, domin karin bayani kan dalilan jinkirin da kuma gabatar da tsare-tsaren biyan bashin da ake binsu.

Google search engine

Wannan matakin na Majalisar ya biyo bayan amincewa da wani kudiri na gaggawa da dan majalisa Hon. Ezechi Nnamdi daga mazabar Ndokwa ta Jihar Delta ya gabatar yayin zaman majalisar.

A cikin kudirinsa, dan majalisar ya nuna damuwa kan yadda da dama daga cikin ma’aikatu da hukumomin gwamnati ba su samu ko rabin kason kasafin kudin ayyukan ci gaba na shekarar 2024 ba, duk da cewa akwai kudin da aka ware a kasafin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mutanen kauyen da suka sayar da buhunan masara don hada N40m suka biya kudin fansa, aka karbi kudin aka kuma ki sako mutanen a...

Dattawan al’ummar Gidan Waya da ke ƙaramar hukumar Lere a jihar Kaduna sun bayyana cewa sun sayar da buhunan masara sama da 3,000 domin tara...

Sojoji sun amince an kitsa yunkurin juyin mulki kan Tinubu

Rundunar sojin Najeriya ta amince cewa wasu jami’anta sun kitsa yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne...

Mafi Shahara