DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilai ta gayyaci ministocin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki da gwamnan CBN kan kin biyan ‘yan kwangila tun Oktoban 2024

-

Majalisar Wakilai ta Tarayya a ranar Alhamis ta gayyaci Ministan Kudi kuma Ministan na tarayya, Wale Edun; ministan tsare-tsaren tattalin arziki da kasafin kudi, Sanata Atiku Bagudu; da kuma Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Olayemi Cardoso, domin bayyana dalilin kin biyan ’yan kwangilar da suka yi aiki da ma’aikatun gwamnati tun daga watan Oktoban shekarar 2024.

Hakazalika, Majalisar ta gayyaci Akanta-Janar na Tarayya da Audita-Janar domin su bayyana tare da sauran jami’an gwamnati a gaban Majalisar a ranar Talata, 13 ga watan Mayu, domin karin bayani kan dalilan jinkirin da kuma gabatar da tsare-tsaren biyan bashin da ake binsu.

Google search engine

Wannan matakin na Majalisar ya biyo bayan amincewa da wani kudiri na gaggawa da dan majalisa Hon. Ezechi Nnamdi daga mazabar Ndokwa ta Jihar Delta ya gabatar yayin zaman majalisar.

A cikin kudirinsa, dan majalisar ya nuna damuwa kan yadda da dama daga cikin ma’aikatu da hukumomin gwamnati ba su samu ko rabin kason kasafin kudin ayyukan ci gaba na shekarar 2024 ba, duk da cewa akwai kudin da aka ware a kasafin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara