DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rukunin farko na Alhazan jihar Kebbi guda 420 sun tashi zuwa Madinah

-

Rukunin farko na maniyyata 420 daga jihar Kebbi sun tashi daga filin jirgin sama na Sir Ahmadu Bello International Airport da ke Birnin Kebbi, zuwa birnin Madina na kasar Saudiyya.

Mataimakin gwamnan jihar Kebbi Sanata Umar Abubakar Tafida wanda ya wakilci Gwamna Nasir Idris, tare da Amirul Hajj na Kebbi Kuma Sarkin Argungu, Alhaji Sama’ila Muhammadu Mera da Shugaban Hukumar jin dadin alhazai ta Jihar Kebbi, Faruq Aliyu Yaro Enabo su ne suka yi wa maniyyatan bankwana.

A jawabansu daban-daban, sun yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa goyon bayan da ya bayar, wajen tabbatar da fara jigilar alhazai cikin sauki.

Amirul Hajj ya tabbatar da cewa an kamala dukkan shirye-shiryen jigilar maniyyatan Kebbi 3,800 da suka hada da ba da fasfo, biza, ga maniyyata daga kananan hukumomi 21 na jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan...

Gwamnatocin Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta a Asabar dinnan

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar ya sanar a shafinsa na X cewa, kasashen sun amince da Shirin tsagaita wuta cikin gaggawa. Shugaba Trump ya sanar...

Mafi Shahara