Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya bayyana cewa gwamnati ba za ta sauya matsayinta kan cire tallafin mai da hada darajar naira ba, domin ceto tattalin arziki.
A rahoton da jaridar Daily Trust ta fitar ya ce cire tallafi ya kawo karshen dogaro da NNPC kadai da kuma karancin mai, yayin da hada darajar naira ya dakile cin moriyar ‘yan tsiraru masu sayar da dala a kasuwar bayan fage.
Onanuga ya amince cewa akwai tsadar rayuwa, amma gwamnati ta dauki matakai don rage radadi, ciki har da dokar ta-baci kan abinci da saukaka shigo da magunguna.
