DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An gurfanar da ‘yan kasar waje 113 akan laifukan yanar gizo da shigowa Nijeriya ba bisa ka’ida ba

-

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ce ta gurfanar da wasu ‘yan kasar waje 113 da laifukan da suka shafi yanar gizo, wadanda suka hada da zamba da safarar kudade da dai sauran su. 
Wani bayani da mai magana da yawun rundunar ya wallafa a shafinsa na X, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ofishin rundunar ‘yan sanda mai yaki da laifukkan yanar gizo ne ya kama mutanen a ranar 3 ga watan Nuwamban 2023 a birnin tarayya Abuja.
Wadanda aka kama a yayin sammen, na fuskantar zarge-zarge ciki har da wadanda suka shafi shige da fice da kuma safarar bil adama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar da ta sake yin nasara. Wannan mataki ya...

Likitoci sun tsunduma yajin aiki kan karancin albashi a Ingila

Dubban likitoci a Ingila sun fara yajin aiki na kwanaki biyar a ranar Juma’a saboda rashin gamsuwa da albashi da kuma karancin guraben horaswa, lamarin...

Mafi Shahara