Rundunar sojin Najeriya na ci gaba da mamayar maboyar fitaccen shugaban barayin daji Bello Turji, bayan ajalin babban abokinsa a ta’addanci Kachalla Kallamu a gagarumin samamen da sojojin runduna ta 8 suka kai a Sabon Birni, Jihar Sokoto.
Majiyar soja ta tabbatar cewa an yi ajalin Kallamu ne tare da hadin guiwar ’yan sa-kai a Kurawa, inda sojoji suka kuma hallaka wani babban mai samar wa Turji kayan aiki.
Kallamu, ɗan asalin Garin-Idi, ya jima ya na hargitsa yankin gabashin Sokoto ta hanyar daukar rayuka, garkuwa da mutane da kuma ka hari a kauyuka, inda yake da kimanin mayaka 100 a karkashinsa.
Wani masanin harkokin tsaro Farfesa Murtala Ahmed Rufa’i ya shaida wa Daily Trust cewa duk da Rashin Kallamu ayyukan Turji na iya ci gaba, kasancewar ba ya cikin manyan kwamandojin sa kai tsaye, domin yana biyayya ga Sa’idu Malam wato Sa’idu Buzu, na biyu a matsayin mataimakin Turji kuma surukinsa.
