DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba ni da wata nadamar goyon bayan Tinubu tun 2022 – Nyesome Wike

-

Ministan Abuja a Nijeriya, Nyesom Wike, ya ce bai taɓa yin nadamar bayyana goyon bayansa ga Shugaba Bola Tinubu tun kafin zaɓen 2023 ba, yana mai jaddada cewa matsayinsa bai sauya ba kafin zaɓe, lokacin zaɓe da kuma bayan kammala zabe.

Wike ya bayyana hakan ne yayin wani taro na musamman da aka shirya domin cika shekarunsa 58 a gidansa da ke Abuja, inda ya ce ya tsaya tsayin daka kan goyon bayan Tinubu bisa ƙa’idar gaskiya, adalci da kuma ra’ayinsa na cewa mulki ya kamata ya koma Kudu.

Google search engine

Tsohon gwamnan Jihar Rivers ya ce shi kaɗai ne daga manyan ’yan adawa da suka fito fili suka mara wa Tinubu baya a wancan lokaci, yana mai cewa sakamakon zaɓe a Rivers ya nuna irin tasirinsa, inda APC ta lashe zaɓen shugaban ƙasa, yayin da PDP ta yi nasara a sauran matakai.

Manyan ’yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban sun halarci taron domin taya Wike murna, tare da yaba rawar da yake takawa a siyasar Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Shehu Sani ya karyata El-Rufai kan batun bacewar Dadiyata

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Comrade Shehu Sani, ya karyata ikirarin tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, cewa Abubakar Idris wanda aka fi sani da...

Mafi Shahara