Tuesday, April 7, 2026
HomeBabban LabarinmuBa ni da wata nadamar goyon bayan Tinubu tun 2022 - Nyesome...

Ba ni da wata nadamar goyon bayan Tinubu tun 2022 – Nyesome Wike

Ministan Abuja a Nijeriya, Nyesom Wike, ya ce bai taɓa yin nadamar bayyana goyon bayansa ga Shugaba Bola Tinubu tun kafin zaɓen 2023 ba, yana mai jaddada cewa matsayinsa bai sauya ba kafin zaɓe, lokacin zaɓe da kuma bayan kammala zabe.

Wike ya bayyana hakan ne yayin wani taro na musamman da aka shirya domin cika shekarunsa 58 a gidansa da ke Abuja, inda ya ce ya tsaya tsayin daka kan goyon bayan Tinubu bisa ƙa’idar gaskiya, adalci da kuma ra’ayinsa na cewa mulki ya kamata ya koma Kudu.

Tsohon gwamnan Jihar Rivers ya ce shi kaɗai ne daga manyan ’yan adawa da suka fito fili suka mara wa Tinubu baya a wancan lokaci, yana mai cewa sakamakon zaɓe a Rivers ya nuna irin tasirinsa, inda APC ta lashe zaɓen shugaban ƙasa, yayin da PDP ta yi nasara a sauran matakai.

Manyan ’yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban sun halarci taron domin taya Wike murna, tare da yaba rawar da yake takawa a siyasar Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata