DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya na bin diddigin shafukan sada zumunta na ‘yan bindiga

-

Gwamnatin tarayya ta ce tana sane da yadda shafukan ‘yan ta’adda ke kara bazuwa a kafafen sada zumunta na zamani a cikin ‘yan kwanakinnan.
Wannan na zuwa ne yayin da ayyukan ‘yan bindiga ke kara karfi a shafukan sada zumunta musamman Tiktok, inda su ke nuna bindiogogi da kuma kudade zube birjik tare da yin barazanar cewa sun fi karfin gwamnati.
A wata hira da jaridar Punch, kodinetan cibiyar yaki Da ta’addanci da ke karkashin ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj. Gen. Adamu Laka, ya ce gwamnati na aiki tukuru domin ganin ta yaki ‘yan ta’addan ta wannan hanyar da suka ɓullo da ita.
Kodinetan ya kira ‘yan bindigar matsorata inda kalubalance su da su fito a yi gaba da gaba da jami’an tsaro ba wai labewa suna barazana ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar shugaban kasa ta mayar wa Atiku martani cewa babu yunwa a Niijeriya

Fadar shugaban kasa ta ce gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na tafiya kan madaidaiciyar hanya, tana mai musanta ikirarin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da...

Kotu ta daure wani dan Nijeriya a Amurka kan laifin zambar kudin gado

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai suna Ehis Lawrence Akhimie hukuncin daurin shekaru fiye da takwas bayan an same shi...

Mafi Shahara