Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuTinubu ya ziyarci jihar Borno domin bude ayyuka

Tinubu ya ziyarci jihar Borno domin bude ayyuka

Shugaba Tinubu, ya ziyarci Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin ƙaddamar da manyan ayyuka da halartar bikin auren ɗan tsohon gwamnan jihar, Sanata Ali Modu Sheriff.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN ya rawaito cewa jirgin shugaba Tinubu ya sauka a filin jirgin sama na Janar Muhammadu Buhari, Maiduguri, da misalin karfe 12:55 na rana.

Ana sa ran ziyarar za ta haɗa da ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnatin jihar da ta tarayya suka aiwatar, tare da halartar taron bikin aure kafin shugaban ƙasar ya ci gaba da sauran tafiye-tafiyen da aka shirya zai yi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata