Wednesday, April 8, 2026
HomeUncategorizedMai neman yi wa kansa kofar rago ne kawai zai yi takara...

Mai neman yi wa kansa kofar rago ne kawai zai yi takara da Tinubu a 2027 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa mai neman yi wa kansa kofar ragone kawai zai tsaya takarar shugaban kasa da shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Shettima ya fadi hakan ne a yayin taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC da ya gudana a ranar Juma’a,inda ya jaddada cewa duk da dimokuradiyya ta ba kowane dan kasa damar tsayawa takara, yanayin siyasar da ke tafe zuwa 2027, ya bayyana karara cewa shugaba Tinubu ke da nasara.

A cewarsa, irin nasarorin da gwamnatin Tinubu ke samu, tare da karfin jam’iyyar APC da goyon bayan da shugaban kasa ke da shi a fadin Nijeriya, sun nuna cewa ‘yan adawa ba su da wata dama ta mai kyau a zabe mai zuwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata