Wednesday, April 8, 2026
HomeKetareAn mika tutar rundunar haɗin gwiwa ta kasashen AES, Nijar, Mali da...

An mika tutar rundunar haɗin gwiwa ta kasashen AES, Nijar, Mali da Burkina Faso

Shugaban mulkin sojin Mali kuma shugaban kungiyar AES, Janar Assimi Goïta, ya jagoranci bikin miƙa tutar rundunar haɗin gwiwar ta kasashen AES a wani biki na musamman da aka gudanar a Bamako a ranar Asabar, 20 Disamba, 2025.

Bikin ya samu halartar manyan jami’an tsaro da wakilan ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar, inda aka bayyana miƙa tutar a matsayin matakin da ke nuna fara aiki tare na rundunar haɗin gwiwar AES domin tsaurara tsaro da kare yankin Sahel.

Matakin na da nufin inganta tsaro tare da aiki da jami’an hadin gwiwa na kasashen domin fuskantar matsalar tsaro da ke addabar yankin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata