DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tarin bashin da kake ciyowa ke jikkata tattalin arzikin Nijeriya, sakon Atiku Abubakar ga Shugaba Tinubu

-

Google search engine

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya ce tarin bashin da gwamnatin APC ke ciyowa na kassara tattalin arzikin kasar.

Atiku ya kuma zargi majalisar dokoki ta kasar da zama taimakawa wajen jefa kasar cikin bashi.

Da yake martani kan bashin da majalisar ta amince Tinubu ya ciyo na baya-bayannan, Atiku ya ambato wani rahoto na bankin duniya wanda ya ce ya dora Nijeriya a mataki na uku cikin kasashen da tulin bashi ya yi wa yawa.

Tsohon shugaban ya bayyana damuwa aka yadda gwamnatin ke ci gaba da cin bashi, duk da cewa a watan Yuli shugaba Tinubu ya ce hukumar tattara haraji ta kasa da hukumar kwastam sun samar da kudade ga kasar wadanda ba a taba gani ba.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya daga Benue ya fice daga PDP zuwa APC

Dan majalisar wakilan Nijeriya mai wakiltar Apa/Agatu da ke jihar Benue, Ojoma Ojotu ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa APC. Bayanin sauya shekar dan...

Vincent Kompany ya tsawaita kwantiraginsa da Bayern Munich

Kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich ta amince da tsawaita kwantiragin Vincent Kompany a matsayin mai horas da tawagar 'yan wasanta.   Jaridar Punch ta ruwaito cewa...

Mafi Shahara