DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun halaka mutum biyar tare da kona shaguna a Zamfara

-

 

Google search engine

Wasu ‘yan bindiga da suka kai hari a kauyen Dayau na karamar hukumar Kaura Namoda a jihar Zamfara sun yi ajalin mutam biyar tare da kona wasu gidaje da shaguna da rumbun ajiyar abinci da dama a kauyen. 

Wani mazaunin garin mai suna Shamsu, ya shaida wa jaridar Premium times cewa ‘yan bindigar sun shafe kusan sa’o’i bakwai suna cin karen su ba babba ka.

Ya kara da cewa yan bindigar sun shigo garin ne ta hanyar Kungurki a kan babura, amma ‘yan banga da jami’an tsaron al’umma sun shafe sama da sa’a day sun na arangama kafin yan yan bindigar su gudu.

Mutumin ya ce bayan sun sake dawowa ne suka shammaci jami’an, inda wasu suka riƙa harbin mai uwa da wabi wasu kuma suka kona gidaje da shaguna.

Duk kokarin da Premium Times ta yi na jin ta bakin jami’in yada labarai na rundunar yan sandan jihar Zamfara hakan ya ci tura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon kwamishinan Ganduje ya soki gwamnatin Abba bisa zargin sayar da filin makarantar

Tsohon kwamishinan ilimi na a zamanin Ganduje, Muhammad Sanusi Sa'id Kiru, ya soki matakin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da Makarantar Sakandare ta ‘Yan...

Hukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar da sahihin zabe

Shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya bayyana aniyarsa ta yin aiki tare da Majalisar Dokoki domin tabbatar da gudanar da sahihin...

Mafi Shahara