Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedTinubu ya umarci a tsananta bincike kan batun hallaka mata da yaranta...

Tinubu ya umarci a tsananta bincike kan batun hallaka mata da yaranta a Kano

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan kisan wata mata, Fatima Abubakar, da ’ya’yanta shida da aka yi a Unguwar Dorayi Chiranci da ke jihar Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba Shugaban shawara kan harkokin yaɗa Labarai Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Litinin, inda Shugaban ya yi Allah-wadai da kisan, yana mai kiran lamarin da mummunan ta’addanci, tare da ta’aziyya ga iyalan mamatan.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa ’yan sanda bisa saurin cafke waɗanda ake zargi, tare da umartar hukumomin tsaro su tabbatar da ingantaccen bincike da gurfanar da su gaban shari’a.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata