DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Kano Abba Kabir Yusuf ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa nuna tausayi da ya yi ga ‘yan Nijeriya

-

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa amsa kiran da jama’a suka yi masa tare da sakin yara 76 da aka tsare, wadanda aka kama bayan zanga-zangar watan Agustan 2024.

Google search engine

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a Talatar nan, Gwamnan ya nuna matukar jin dadinsa da tausayin da shugaban kasar ya nuna, wanda ya bayyana shi a matsayin wani gagarumin abin alfahari ga matasan jihar Kano.

Gwamna Abba ya godewa shugaba Tinubu bisa fahimtarsa ​​da kuma baiwa yaran dama.Yara 76 da aka tsare saboda zanga-zangar da aka yi a watan Agusta, za a dawo da su Kano inda za a duba lafiyarsu tare da samun kulawar da ya dace kafin a sada su da iyayen su.

Gwamna Yusuf ya kuma ba da tabbacin cewa za a mayar da yaran cikin al’umma da kuma shigar da su makarantu, tare da samar musu da damar sake gina rayuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara