Tuesday, April 7, 2026
HomeBabban LabarinmuGwamnatin Nijeriya ta dora laifin talaucin 'yan kasar kan gwamnoni da kananan...

Gwamnatin Nijeriya ta dora laifin talaucin ‘yan kasar kan gwamnoni da kananan hukumomi

Fadar shugaban Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatocin jihohi da kuma kananan hukumomi ne silar fadawar ‘Yan Nijeriya miliyan 133 cikin kangin talaucin da suke fama da shi a yanzu.

Wata sanarwa da hadimin shugaba Tinubu, Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na X ce ta bayyana hakan, inda ya ce kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bai wa jihohi da kananan hukumomi ikon samar da duk wasu bukatu na cire al’umma daga talauci.

Kazalika ya ce babu wani sashe a kundin tsarin mulki da ya dora wa gwamnatin tarayya nauyin fitar da al’ummar Nijeriya daga talauci, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Ya kuma soki yadda ya ce gwamnatocin jihohi na watsi da muhimman ayyuka tun daga tushe irin su kiwon lafiya da kuma ilimi, tare da cewa hakan na ruruta wutar kangin talauci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata