Tuesday, April 7, 2026
HomeSiyasaShugaba Tinubu ya sasanta rikicin Wike da Fubara a Abuja

Shugaba Tinubu ya sasanta rikicin Wike da Fubara a Abuja

Shugaba Bola Tinubu ya shiga tsakani wajen sasanta rikicin siyasa a jihar Rivers, inda suka gana da Gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, da Ministan Abuja Nyesom Wike, a fadar shugaban kasa, a daren Litinin.

Jaridar The Nation, ta ruwaito cewa Shugaba Tinubu ya gana da shugabannin jihar Rivers ciki har da Wike da Fubara, tare da wasu shugabannin siyasa daga jihar.

Rahotanni sun bayyana cewa Fubara ya yi alkawarin nuna girmamawa ga Wike a nan gaba, alamar cewa rikicin siyasa tsakanin manyan ‘yan siyasar jihar na iya samun sassauci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata