DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya za ta yi zaman gaggawa kan jadawalin zaben 2027

-

Majalisar Wakilan Nijeriya za ta koma zama ranar Talata, 17 ga Fabrairu, domin tattauna batutuwan zabe da suka taso bayan sanar da jadawalin zaben 2027 da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fitar.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya sanar da cewa za a gudanar da zaben Shugaban Kasa da na Majalisar Tarayya ranar 20 ga Fabrairu, 2027, yayin da zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi zai gudana ranar 6 ga Maris, 2027, bisa tanadin kundin tsarin mulki da Dokar Zabe ta 2022.

Google search engine

Sanarwar zaman gaggawar ta fito ne ta hannun kakakin majalisar, Rep. Akin Rotimi Jr., wanda ya ce matakin na nuna kudurin majalisar na daukar mataki kan duk wani abu da ya shafi tsarin dimokuradiyya.

Haka kuma, Ofishin Kakakin Majalisar ya bayyana cewa zaman zai ba da damar sake duba kudirin gyaran dokar zabe, musamman batun rage wa’adin sanar da zabe daga kwanaki 360 zuwa 300, domin ba da sassauci wajen tsara ranakun zabe duba da cewa wasu daga cikin ranakun sun yi daidai da watan Ramadan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara