DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin ministocin da shugaba Bola Tinubu ya nada

-

 

Majalisar Dattawan Nijeriya

A yau ne majalisar dattawa za ta tantance ministocin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika mata domin tantance su.

Daily Trust ta ruwaito cewa hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi bincike tare da wanke wadanda aka nada, gabanin tantance su a yau.

A satin da ya gabata ne dai Tinubu ya yi wa majalisar ministocinsa garambawul, inda ya kori ministoci shida tare da nada wasu sabbi bakwai.

Daily Trust ta ruwaito cewa, a ranar litinin wadanda aka nada sun sun je ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin majalisar dattawa, Sanata Basheer Lado, domin gabatar da takardunsu.

Sanata Lado, a wata sanarwa da ya fitar, ya tabbatar da cewa, wadanda aka nada a matsayin ministocin, majalisar dattawa, za ta fara tantance su yau a harabar majalisar a Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cin hanci la’ana ce, mu tsabtace kanmu daga rashawa- EFCC

A wani sakon tunatarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook albarkacin ranar Juma’a, hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya,...

Babu karar-kwana, da tuni na bakuncin lahira a zanga-zangar #EndSARS – Jarumi a Nollywoood Desmond Elliot

Fitaccen ɗan wasan fina-finan Nollywood kuma ɗan siyasa, Hon. Desmond Elliot, ya bayyana yadda ya kuɓuta daga wani hari da wasu baƙin fuska suka yi...

Mafi Shahara