Tuesday, April 7, 2026
HomeUncategorizedSuper Eagles ta fãsa buga wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin...

Super Eagles ta fãsa buga wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afirka

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ta yanke shawarar janye Super Eagles daga wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta 2025 da za tayi da Libiya a ranar talata.

Hakan ya biyo bayan yanayi Mai cike da takaici da  tawagar ta shafe sa’o’i12 a filin jirgin saman Al-Abraq na kasar Libiya, yayin da tawagar ta makale bayan wani sauƙa na gaggawa a yammacin Lahadi.

Jaridar Punch ta rawaito cewa tawagar ta Nijeriya na kan hanyar zuwa birnin Benghazi ne domin gudanar da wasan share fage mai matukar mahimman ci, lokacin da jirgin da su ka karba haya ya samu matsala .

Lamarin da ba zato ba tsammani ya sa ‘yan wasa da jami’ai suka makale ba tare da wani taimako daga hukumar kwallon kafa ta Libiya ba, abin da ya fusata kungiyar ta NFF.

NFF  ta cigaba da cewa yan wasan sun gaji saboda haka ne sun yanke shawarar ba za su buga wasan ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata