Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada kudurinsa na kare dimokuradiyya da bin doka a Nijeriya, yana mai cewa shi “dan dimokuradiyya ne na gaske”.
Ya bayyana hakan ne yayin buda baki da shugabannin jam’iyyar APC da kuma majalisar shawarwari tsakanin jam’iyyu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Tinubu ya ce dimokuradiyya a Nijeriya ta samu ne bayan doguwar gwagwarmaya, inda wasu suka shiga zanga-zanga, aka tsare su, wasu ma suka yi gudun hijira.
A cewarsa, shi da sauran masu gwagwarmaya sun tsaya tsayin daka wajen tabbatar da hadin kan Nijeriya da dorewar dimokuradiyya.
Shugaban ya kuma ce ci-gaban dimokuradiyya na bukatar gaskiya da adalci a cikin jam’iyyun siyasa, yana mai jaddada cewa dole ne a mutunta rinjaye tare da bai wa marasa rinjaye damar fadin ra’ayinsu.
Hakazalika, ya kuma tabbatar wa jam’iyyarsa ta APC cewa zai ci gaba da kasancewa tare da ita.
