Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuNi cikakken dan dimokradiyya ne - Shugaba Bola Tinubu

Ni cikakken dan dimokradiyya ne – Shugaba Bola Tinubu

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada kudurinsa na kare dimokuradiyya da bin doka a Nijeriya, yana mai cewa shi “dan dimokuradiyya ne na gaske”.

Ya bayyana hakan ne yayin buda baki da shugabannin jam’iyyar APC da kuma majalisar shawarwari tsakanin jam’iyyu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Tinubu ya ce dimokuradiyya a Nijeriya ta samu ne bayan doguwar gwagwarmaya, inda wasu suka shiga zanga-zanga, aka tsare su, wasu ma suka yi gudun hijira.

A cewarsa, shi da sauran masu gwagwarmaya sun tsaya tsayin daka wajen tabbatar da hadin kan Nijeriya da dorewar dimokuradiyya.

Shugaban ya kuma ce ci-gaban dimokuradiyya na bukatar gaskiya da adalci a cikin jam’iyyun siyasa, yana mai jaddada cewa dole ne a mutunta rinjaye tare da bai wa marasa rinjaye damar fadin ra’ayinsu.

Hakazalika, ya kuma tabbatar wa jam’iyyarsa ta APC cewa zai ci gaba da kasancewa tare da ita.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata