Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuShugaba Trump na Amurka ya bukaci kasashe da su tura jiragen yaki...

Shugaba Trump na Amurka ya bukaci kasashe da su tura jiragen yaki na ruwa don kare mashigin Hormuz

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bukaci wasu ƙasashe su tura jiragen yaƙin ruwa domin taimakawa wajen kare Hormuz, wata muhimmiyar hanyar jigilar man fetur ta duniya da rikicin Gabas ta Tsakiya ya jefa cikin barazana.

Jaridar Punch ta rawaito Trump na bayyana hakan ne a ranar Asabar ta shafinsa na sada zumunta inda ya ce kasashe da dama za su hada kai da Amurka domin tabbatar da cewa mashigin ya kasance a bude ga jiragen ruwa na kasuwanci.

Trump ya kuma yi kira ga manyan ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziki kamar China, Faransa, Japan, Koriya ta Kudu da Birtaniya su tura jiragen ruwa zuwa yankin, ganin cewa su ma rikicin da ake samu na iya shafar tattalin arzikinsu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata