Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedINEC ta dakatar da shirin tabbatar da rajistar masu zabe a fadin...

INEC ta dakatar da shirin tabbatar da rajistar masu zabe a fadin Nijeriya

Hukumar zaɓen Nijeriya, INEC ta umurci dukkan kwamishinonin zaɓe na jihohi da su dakatar da duk wani shiri da ya shafi aikin sabunta katin zaɓe da aka tsara gudanarwa a faɗin ƙasar.

Jaridar The Guardian ta rawaito cewa wannan umarni na kunshe ne a cikin wata takarda da sakatariyar hukumar, Rose Oriaran-Anthony, ta sanya wa hannu, inda aka buƙaci a dakatar da dukkan shirye-shirye da wayar da kan jama’a kan aikin har sai an bayar da sabon umarni.

Tun da farko, hukumar ta sanar da cewa za a fara aikin ne daga ranar 13 ga Afrilu, 2026, domin sabunta rijistar masu kaɗa ƙuri’a kafin zaɓen 2027.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata