Tuesday, April 7, 2026
HomeUncategorizedKu rage farashin man fetur, ‘yan Nijeriya na fama da yunwa, Kukah...

Ku rage farashin man fetur, ‘yan Nijeriya na fama da yunwa, Kukah ya fadawa jam;iyyar APC

Ku rage farashin man fetur, ‘yan Nijeriya na fama da yunwa, Kukah ya fadawa jam;iyyar  APC

Babban limamin cocin Katolika na Sokoto, Mathew Hassan Kukah, ya bukaci shugabannin jam’iyyar APC mai mulki da su rage farashin man fetur a halin yanzu, yana mai cewa ‘yan Nijeriya na fama da yunwa.

Ya yi wannan jawabi ne a Juma’ar nan a Abuja, yayin da ake kaddamar da cibiyar ci gaba (TPI).

A ranar Talatar da ta gabata ne farashin man fetur a Nigeriya ya karu daga N855, zuwa N918,a gidajen man ‘yan kasuwa kuwa ana sayar da man N1000,zuwa 1200 a cikin kasar.

Kukah ya ce,‘yan Nijeriya jin yunwa, ya kamata a  nemo hanyar rage farashin man fetur a wannan lokaci.

Ya ce mu tuna da cewa idan har ba a kafa dimokuradiyya a kan ingantaccen tushe ba, to za mu yi gini a kan yashi, don haka ya kamata mu gyara matsalar dimokradiyya a Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata