Thursday, April 9, 2026
HomeUncategorizedSERAP ta kai karar Akpabio, Abbas kotu kan zargin yanka wa kansu...

SERAP ta kai karar Akpabio, Abbas kotu kan zargin yanka wa kansu alawus mai gwabi

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaki da cin hanci a Nijeriya ta maka shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas gaban kotu kan kawo karshen kayyade alawus-alawus dinsu.

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya yi zargin cewa ‘yan majalisar su ke yanke na kansu albashi da alawus-alawus.

Sai dai Majalisar ta musanta wannan zargi.

A cikin karar da aka shigar mai lamba: FHC/ABJ/CS/1289/2024 a ranar Juma’ar da ta gabata a babbar kotun tarayya da ke Abuja, SERAP na neman da a tilasta wa Akpabio da Abbas su kawo karshen wannan lamari na kayyade albashi da alawus-alawus.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata