Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedMamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a jihar Maradi dake janhuriyar...

Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a jihar Maradi dake janhuriyar Nijar ya yi sanadin rayukan mutane da dama

Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a jihar Maradi dake janhuriyar Nijar ya yi sanadin rayukan mutane da dama

Saukar ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka samu a ranar juma’ar nan da ta gabata ya yi sanadin rayukan mutane da dama tare da jikkata wasu masu yawan gaske.

Rahotanni da wadansu fefen bidiyo da ake yadawa a shafukan sada zumunta na zamani na nuni da yadda ruwan ya yi awan gaba da dukiyoyin al’ummar garin Maradin da kewaye.

Kazalika ambaliyar da mazauna garin ke cewa ba a taba ganin irin ta ba a tarihi ta yi sanadiyyar lalacewar hanyoyi da rubtawar gidaje masu tarin yawa.

Ko da yake a hukumance ba a sanar da adadin asarar da ake fuskanta da rayukan ba amma wasu rahotanni na nuni da cewa mutum 14 ne suka hallaka a cikin wannan ambaliya yayin da kadarori da dukiyoyin al’umma na a kalla bilyoyin Cfa ne suka tafi a cikin ruwan.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata