DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An hallaka jami’an ‘yan sanda yayin zanga-zangar ‘yan shi’a a Abuja

-

An harbe wani dan kasuwa, tare kashe wasu ‘yan sanda biyu a wani yamutsi da ya kaure tsakanin jami’an ‘yan sanda da mabiya mazhabar Shi’a a kasuwar Wuse da ke Abuja.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, an harbi dan kasuwar mai suna Amiru na gudun ceton ransa, yayin da wani alburushi ya same shi a kirji, a lokacin da ‘yan sanda ke korar masu zanga-zanga na mabiya mazhabar Shi’a a Wuse zone 6, Abuja.

Kazalika, bayanai sun ce an kone motocin ‘yan sanda uku a yayin yamutsin.

Mabiya mazhabar Shi’a din dai na muzaharar Arbaeen don cika kwanaki 40 na bikin Ashura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

George Akume Har Yanzu Shi Ne Sakataren Gwamnatin Tarayya – Fadar Shugaban Kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF). A wata sanarwa da mai...

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Mafi Shahara