DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a bude sashen da zai rika duba lafiyar shugaban kasa da sauran manyan kasa a babban asibitin Nijeriya da ke Abuja

-

Asibitin kasa da ke Abuja zai bude wani sashe na musamman wanda zai kula da shugabanni, manyan jami’an gwamnati, da sauran shahararrun mutane dake ciki da wajen kasar.
Babban daraktan asibitin, farfesa Mahmud Raji, ya bayyana hakan jiya a Abuja yayin da ya jagoranci wata tawaga zuwa hedkwatar Media Trust Group.
Farfesa Muhammad ya ce za a gina wani gidan zama ko masauki da aka hade da sashen na musamman wanda zai kasance kamar otal mai tauraro biyar ko bakwai domin kula da dukkan nau’ikan manyan baki.
Farfesa Raji ya kuma ce sashen na musamman zai samu dakin gwaje-gwaje na ilimin guba, yana mai cewa a halin yanzu babu wani asibitin gwamnati da ke da irin wannan dakin gwaje-gwajen domin gwajin guba daga abinci ko muhalli a yayin gaggawa ga shugabannin da ke ziyara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Murabus din Ganduje wata maƙarƙashiya ce aka shirya domin cire Shettima daga gwamnatin Tinubu – Zargin wasu mutanen Borno

Wasu daga cikin al'ummar jihar Borno sun zargi murabus din Ganduje a matsayin wata maƙarƙashiya da aka shirya domin a kawar da Kassim Shettima a...

Mafi Shahara