Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedMatasa za su ci moriyar gwamnatin Tinubu - Shettima

Matasa za su ci moriyar gwamnatin Tinubu – Shettima

 Matasa za su ci moriyar gwamnatin Tinubu – Shettima 

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya jaddada kudirin gwamnatin shugaba Bola Tinubu na tallafawa da karfafawa matasa ‘yan Najeriya kwarin guiwa wajen yin fice a sana’o’in da suka zaba.

 A cewarsa, shugaban kasa yana mutunta matasan Najeriya, kuma jajircewarsa na bayyana a cikin nade-naden mukaman da ya yi da kuma manufofin gwamnati da tsare-tsare irin su asusun zuba jari na matasa, iDICE Programme, da bankin raya matasa na kasa da dai sauransu.

 Mataimakin shugaban kasar ya yi wannan jawabi ne a ranar Juma’a a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar matasan jam’iyyar APC, karkashin jagorancin shugaban matasan jam’iyyar na kasa Dayo Israel, a ziyarar ban girma da suka kai fadar shugaban kasa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata