Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedZa mu dauki Tinubu aiki a matsayin daraktan yakin neman zaben PDP...

Za mu dauki Tinubu aiki a matsayin daraktan yakin neman zaben PDP a 2027 – Bala Muhammed

Gwamna Bala Muhammad na jihar Bauchi ya ce jam’iyyar PDP za ta dauki shugaba Tinubu aiki ya zama Daraktan yakin neman zaben jam’iyyar PDP a babban zaben kasar na shekarar 2027.

Bala Muhammed ya bayyana haka ne a wajen kaddamar da yakin neman zaben kananan hukumomin jam’iyyar PDP a jihar a gidan gwamnati da ke Bauchi a ranar Laraba.

“Akwai yunwa a kasa  kuma mutane sun fara fushi. Dole ne mu magance matsalolinmu na ci gaba.  Babu aikin yi a ko’ina, tsarin ilimin mu ba ya aiki, kuma sabbin manufofin gwamnatin tarayya ba sa aiki.

 “Dole ne su fahimci cewa shirin su ne ya haifar da wadannan matsaloli.  A madadin ku, ina gaya wa Shugaba (Bola) Tinubu ya canza manufofinsa saboda ba sa aiki ko kadan. Inji Gwamnan na jihar Bauchi

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata