Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedGwamnan Kano ya mika sunan karin kwamishina ga majalisar dokokin jihar domin...

Gwamnan Kano ya mika sunan karin kwamishina ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa

Gwamnan Kano ya mika sunan karin kwamishina ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya mika karin mukamin kwamishina ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa.

kakakin majalisar, Alhaji Jibrin Falgore, ya karanta wasikar da gwamnan ya aike wa majalisar yayin zaman ta a talatar nan.

Ya ce wanda aka nada shi ne Muhammad Inuwa-Idris, Manjo-janar mai ritaya.Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini Dala, ya ce tantancewa tare da tabbatar da wanda aka mika sunan nasa zai kawo ci gaban jihar baki daya.

Yace wanda aka nada zai taimaka wa gwamnati wajen aiwatar da wasu manufofi da shirye-shiryenta kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Daga nan sai shugaban majalisar ya bukaci wanda aka zaba ya bayyana a gaban majalisar a ranar Laraba domin tantancewa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata