Thursday, April 9, 2026
HomeUncategorizedTinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin APC kan batun zanga-zanga

Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin APC kan batun zanga-zanga

Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin APC kan batun zanga-zanga 

Shugaba Bola Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC karkashin kungiyar gwamnonin Progressives Forum a fadar sa da ke Abuja.

Taron wanda aka fara da misalin karfe 1, ya biyo bayan kiraye-kirayen da ake yi na zanga-zangar adawa da matsalar tattalin arziki a fadin Nijeriya.

Ko da yake ba a san ajandar taron ba, amma ana iya danganta shi da zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a ranar 1 – 10 ga Agusta.

Zanga-zangar wacce aka shirya a karkashin taken ‘EndBadGovernance’ ta samu karbuwa sosai a shafukan sada zumunta duk da cewa wadanda suka shirya zanga-zangar ba a bayyana sunansu ba,kuma ba babu sunan wata kungiya da ta dauki nauyi a hukumance ba.

Wannan taron ya biyo bayan kammala taron kungiyar gwamnonin Nijeriya da aka yi a daren Larabar da ta gabata, kuma ya biyo bayan soke taron Majalisar Tattalin Arzikin kasa da aka shirya gudanarwa a yammacin ranar Alhamis dinnan.

Wadanda suka hallarci taron sun hada da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ministan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Wale Edun da Abubakar Bagudu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata