Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedZa a rika ba mata hutun 'ta-kaba' idan mazajensu sun rasu a...

Za a rika ba mata hutun ‘ta-kaba’ idan mazajensu sun rasu a Katsina

Za a rika ba mata hutun ‘ta-kaba’ idan mazajensu sun rasu a Katsina

Gwamnatin jihar ta bullo da sabon tsarin ba mata ma’aikatan da mazajensu suka rasu hutun watanni hudu da kwanaki 10 don su yi ‘ta-kaba’ a jihar.

Musulunci dai ya tanadi ‘ta-kaba’ ga matan da mazajensu suka rasu su zauna gida a killace don jimamin rasuwar mazajen nasu.

Jaridar Punch ta jiyo shugaban ma’aikatan gwamnati a jihar Katsina Falalu Bawale ba cewa an aike da sanarwa ga duk ma’aikatu, sassa da hukumomin gwamnati da su rika ba mata hutun ‘ta-kaba’ idan mazajensu sun rasu.

Hakan dai ya biyo bayan bukatar da majalisar dokokin jihar ta gabatar na neman a samar da tsarin ba da hutun ‘idda’ ga mata ma’aikatan da mazajensu suka rasu, wanda daga bisani sashen zartarwar jihar ya amince.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata