DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda a katsina sun kama wani matashi dake kaiwa ‘yan bindiga bayanai

-

‘Yan sanda a katsina sun kama wani matashi dake kaiwa ‘yan bindiga bayanai

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta kama wani matashi dan shekara 13 da ake zargin yana bayar da bayanai ga ‘yan bindiga.

Google search engine

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ASP Abubakar Sadiq-Aliyu ya bayyana hakan a Katsina.

A ranar 3 ga watan Yuli, rundunar ‘yan sandan tare da hadin guiwar ‘yan kungiyar sakai a jihar da ke kauyen Dansoda a karamar hukumar Dandume sun yi nasarar cafke matashin mai shekaru 13.

An kama wanda ake zargin ne bayan samun bayanan sirri kan munanan ayyukansa. Ya kware wajen bayar da bayanai ga ‘yan bindigar.

A yayin gudanar da bincike, ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa, sannan kuma ya ambaci wani Abba, wanda a yanzu haka yake a matsayin wanda ya taimaka masa.

Rundunar ta kuma yi nasarar cafke wani Musaddik Abdullahi da ke zaune a unguwar Kofar Kaura a Katsina, mamban wasu mutane hudu da suka yi kaurin suna wajen garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara