Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedEl-Rufai ya maka wani dan majalisa a Kaduna da gidan talabijin na...

El-Rufai ya maka wani dan majalisa a Kaduna da gidan talabijin na Channels a kotu

El-Rufai ya maka wani dan majalisa a Kaduna da gidan talabijin na Channels a kotu

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya maka wani dan majalisar dokokin jihar Kaduna, Henry Marah da gidan talabijin na Channels TV a kotu,kan abinda ya kira bata suna da ake yi masa kan binciken bashin naira biliyan 423.

A cikin takardar sammacin da aka shigar a gaban wata babbar kotun a Abuja mai dauke da kwanan wata 11 ga watan Yuli, 2024, El-Rufai, ta hannun lauyansa, A.U. Mustapha (SAN) ya ce hirar da aka yi a gidan Talabijin na Channels TV a ranar 5 ga watan Yuni mai taken “Binciken Gwamnatin El-Rufa’i” anyi ta ne domin bata masa suna.

El-Rufai na neman abiyashi diyyar naira Biliyan 3,kan abinda ya kira rashin gaskiya da kuma bata masa suna.

An jiyo Marah a cikin hirar yana cewa El-Rufai ya ci bashin ne ba tare da bin ka’ida ba kuma ba a san adadin kudaden ba.

Tun da farko El-Rufai ya shigar da karar ne yana mai cewa kwamitin da majalisar dokokin jihar ta kafa kan binciken bashin da ya ciyo wasu kudade,tare da kwangiloli da sauran batutuwan da suka shafi gwamnatin jihar Kaduna daga ranar 29 ga watan Mayu 2015,zuwa 29 ga Mayu 2023, bai yi masa Adalci ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata