DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci gwamnatin Tinubu tayi gaggawar dakatar da yarjejeniyar SAMOA

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci gwamnatin Tinubu tayi gaggawar dakatar da yarjejeniyar SAMOA

Bayan wani kudiri na gaggawa wanda mambobin majalisar wakilai 88, suka suka gabatar, majalisar wakilan ta bukaci gwamnatin tarayya da ta dakatar da aiwatar da yarjejeniyar ta Samoa har sai an gama bincike.

Google search engine

Da yake gabatar da kudirin a ranar Talatar nan, dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Dala a kano, Aliyu Madaki, ya ja hankali kan batun da ke nuna “daidaitan jinsi” tare da duk wasu batutuwa dake dake haifar da cece kuce.

Majalisar ta kuma umarci kwamitocin dake da alaka da yarjejeniya ta kasa da kasa da su binciki kudurorin yarjejeniyar da ke cike da ake ta cece-kuce akai.

Takaddama dai ta kunno kai kan yarjejeniyar Samoa da gwamnatin tarayya ta rattaba hannu da kungiyar Tarayyar Turai, inda da dama suka nuna rashin jin dadinsu kan yadda gwamnatin Nijeriya ta amince da yarjejeniyar.

Yarjejeniyar ta Samoa ta haifar da cece-kuce a yanar gizo tare da wasu da dama da ke adawa da yancin LGBT, wanda ya sabawa dokar hana auren jinsi da ma’auratan da shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kafa a shekarar 2014.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara