DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun gano wasu na kokarin tayar da tarzoma a kano-CP Gumel.

-

Mun gano wasu na kokarin tayar da tarzoma a kano-CP Gumel.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta gano wani shiri na tayar da tarzo ma a jihar kan rikicin masarauta.

Google search engine

Kwamishinan ‘yan sandan Kano,CP Mohammed Usaini Gumel ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a daren Litinin .

Gumel ya ce gwamnatin jihar ta na kokarin daidaita batun masarauta kuma duk wani rashin jituwa ana sa ran za a warware shi a kotu ga duk wanda yake da korafi.

Yace mu a matsayinmu na jami’an tsaro muna tsayawa kan doka kuma za mu aiwatar da ita.

Ya kara da cewa sun samu sahihan bayanai game da bata gari da ke kokarin tayar da tarzoma a wurare, musamman Majalisar Dokoki da sauran muhimman wurare a cikin Jihar, majiyoyi da yawa sun tabbatar da hakan.

Duk wanda ke son ta da tarzoma, jami’an tsaro suna da karfin da za su iya dashi. Mun kammala shirye-shiryen fara sintiri sossai da gano wuraren da aka sanar da mu cewa miyagun na wajen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Mafi Shahara