DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zan ci gaba da tsayawa takarar shugaban kasa,muddin Ina raye-Atiku Abubakar

-

 Zan ci gaba da tsayawa takarar shugaban kasa,muddin Ina raye-Atiku Abubakar

Google search engine

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar, ya sha alwashin ci gaba da tsayawa takara muddin yana cikin koshin lafiya.

Atiku ya bayyana haka ne lokacin da yake hira da sashen hausa na Muryar Amurka a Abuja.

Da yake tsokaci kan rikicin da ke faruwa a jam’iyyarsa ta PDP, ya ce akwai bukatar jam’iyyar ta hada kai tare da kulla kawance da sauran kungiyoyin siyasa domin lashe zaben shugaban kasa a 2027 mai zuwa.

A cikin hirar ta sa Atiku ya ce: tabbas zai ci gaba da tsayawa takara muddin yana da rai da lafiya.

Yace ko da tsohon shugaban Amurka Abraham Lincoln ya yi takara sau bakwai kafin daga bisani ya yi nasara.

To sai dai idan aka yi la’akari da halin da jam’iyyar PDP ke ciki a halin yanzu, a bayyane yake cewa yunkurin hannu daya ba zai wadatar ba wajen lashe zaben. Ana buƙatar goyon baya mai ƙarfi da haɗin gwiwa tare da sauran jam’iyyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mijina (Sani Abacha) bai saci kudin Najeriya ba -Maryam Abacha

Tsohuwar matar shugaban kasa, Maryam Abacha, ta musanta zargin cewa marigayi mijinta, Janar Sani Abacha, ya wawure dukiyar kasa. A wata hira da aka watsa a...

‘Yan sanda a Katsina sun ceto mutane 11 da aka yi yunkurin garkuwa da su

Hadakar 'yan sanda, jami'an tsaron sirri na DSS, sojoji da jami'an C-Watch hade da 'yan banga a jihar Katsina sun yi nasarar kubutar da mutane...

Mafi Shahara