DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Cutar kyanda tayi sanadiyyar mutuwar su yara 49 a jihar Adamawa.

-

Cutar kyanda tayi sanadiyyar mutuwar su yara 49 a jihar Adamawa.

Adadin wadanda suka rasa rayukan su sakamakon kamuwa da cutar kyanda a jihar Adamawa ya kai 49.

Google search engine

Hakan ya fito ne a daidai lokacin da jami’an gwamnatin jihar ke bayar da bayanai kan kokarin dakile cutar yayin da hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta yi jawabi ga manema labarai a birnin Yola kan ka’idojin bayar da rahoto na gaskiya kan cutar.

A yayin taron wayar da kai na WHO a ofishin ta na Yola, masanin cutar kanjamau na jihar Adamawa, Kadabiyu Jones, ya ce kawo yanzu an samu rahoton mutuwar mutane 49, yayin da 143 daga cikin 818 da ake zargin sun kamu da cutar kyanda ya tabbatar da sun kamu da cutar.

Ya ce wadanda abin ya shafa yara ne da ke tsakanin shekara 1 zuwa 14, kuma yawancinsu ba a taba yi musu allurar riga-kafi ba.

Ya tabbatar da cewa jihar ta tura jami’an sa ido domin gano bullar cutar kuma tana aiki tukuru don ganin kawo karshen kamuwa da cutar ta hanyar rigakafin da ake yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara