Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedMatatar mai ta Dangote ta sanar rage farashin man dizal.

Matatar mai ta Dangote ta sanar rage farashin man dizal.

Matatar mai ta Dangote ta sanar rage farashin man dizal.
Makonni kadan da suka gabata, a lokacin da ta fara aiki, matatar mai ta Dangote ta sanya farashin man dizal a kan Naira 1,200.
Yayin da ake fitar da kayayyakin, matatar ta samar a kan farashi na Naira 1,200 ga kowace lita makonni uku da suka wuce.
Hakan ya nuna sama da kashi 30 cikin 100 na raguwar farashin kasuwa a baya na kusan Naira 1,600 kowace lita.
Sai dai a ranar Talata an kara samun raguwar Naira 200 a farashin, inda a yanzu farashin ya kai N1,000.
A ranar Larabar da ta gabata ne shugaban rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya ce rage farashin man dizal zuwa Naira 1,200 zai yi tasiri ga hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya.
Ya yi wannan jawabi ne a wata ganawa da manema labarai bayan ziyarar da ya kai wa Shugaba Bola Tinubu na bikin Sallar a Legas.
A cewar Dangote, an samu ci gaban tattalin arziki a baya-bayan nan, wanda ke nuni da cewa kasar na kan turba mai kyau bisa matakan tattalin arziki da gwamnati ke dauka a halin yanzu.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata