DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama mahaifin da yake lalata da diyarsa budurwa mai shekaru 17 har ta samu ciki a Bauchi

-

 

Jami’an rundunar ‘yan sanda a Jihar Bauchi sun sanar da kame Umar Sule, mai shekaru 54, bisa zargin yin lalata da diyar cikinsa, budurwa mai kimanin shekaru 17 da haihuwa har ta samu ciki.

Google search engine

Kakakin hukumar, Ahmed Wakil, cikin sanarwar da ya fitar, ya ce sun samu korafi daga Abdullahi Baban Karatu, mai shekaru 55, daga kauyen Kurmin Ado, kan zargin da ake yi wa Sule na aikata laifin tare da diyarsa a lokuta daban-daban, wanda ya sabbaba ta dauki ciki na watanni uku, bisa ga rahoton likita.”

Sanarwar ta kara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya umarci a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara