DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sanda Kaduna ta yi nasarar ceto mutane 17 daga hannun masu garkuwa da mutane tare da kwato bindigu 21

-

 

Google search engine

 Jami’an sashin yaki da masu garkuwa da mutane na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, tare da hadin gwiwar ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, sun ceto mutane 17 da aka yi garkuwa da su a ranar 3 ga Maris, 2025, daga Sarkin Pawa, jihar Neja.  

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa wannan nasara na daga cikin kokarin Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya jagoranci jami’an leken asiri da sauran hukumomin tsaro domin magance matsalolin tsaro. A cewar rundunar, an samu bindigogi kirar AK-47 guda 21 a sansanin masu garkuwar da aka kame.  

Daga cikin wadanda aka ceto sun hada da Williams Ubadia, Samuel Ezekiel, Ishaku Ishaya, Rebecca Ezekiel, da Victoria Ishaya, da sauran su. Dukkanin mutanen da aka ceto an kai su asibitin ‘yan sanda da ke Kaduna domin duba lafiyarsu, kuma an tabbatar da cewa suna cikin koshin lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 99 domin rigakafin cutar mahaukacin kare

Gwamnatin jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan 99 domin fara shirin rigakafin cutar mahaukacin kare (rabies), inda ake sa ran yi wa akalla...

Wike ya koka kan ƙarancin masu fitowa zabe a Abuja

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda ake gudanar da zaɓen kananan hukumomi cikin lumana a fadin Abuja, duk da...

Mafi Shahara