Monday, April 6, 2026
HomeUncategorized'Yan sanda sun tabbatar da mummunan harin da 'yan bindiga suka kai...

‘Yan sanda sun tabbatar da mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai a jihar Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da kai hari a kauyen ‘Yar Nasarawa a karamar hukumar Faskari ta jihar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ASP Aliyu Abubakar Sadiq ya aike wa DCL Hausa, ta ce ‘yan bindigar sun kashe mutane 6, sun kuma raunata 10.
Kazalika, sanarwar ta ce ‘yan bindigar sun kone gidaje 3 da motoci kusan 10. Tuni dai jami’an tsaro sun kewaye yankin a yunkurin kama wadanda suka yi wannan aika-aika.
Da sanyin safiyar Talatar nan, DCL Hausa ta ba da labarin cewa wasu ‘yan ta’adda sun farmaki kauyen ‘Yar Nasarawa a karamar hukumar Faskari, inda har suka kone wani mutum da ransa.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata