Tuesday, April 7, 2026
HomeUncategorizedNDLEA ta kama mutane 198 da ake zargi da safarar kwayoyi a...

NDLEA ta kama mutane 198 da ake zargi da safarar kwayoyi a Kano.

 NDLEA ta kama mutane 198 da ake zargi da safarar kwayoyi a Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, reshen jihar Kano, ta ce ta kama wasu mutane 198 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi tare da tarwatsa mahadar da ake tattaruwa don safarar miyagun kwayoyi guda 21 a Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Kakakin hukumar a jihar Kano Sadiq Muhammad-Maigatari ya raba wa manema labarai a Kano.

Ya ce an kama su ne a tsakanin 17 zuwa 26 ga watan Janairu, a cikin shirin hukumar na “Operation Hana Maye” da Kwamandan Hukumar Abubakar Idris-Ahmad ya kaddamar domin yaki da shaye shaye.

A cewarsa, daga cikin mutane 198 da aka kama, 177 maza ne, 21 kuma mata ne.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata